Hadisai arba'in akan falalar sadaka An kar~o daga Abu Musa Al-Ash’ari Allah Ya yarda da shi An kar~o daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce Wajibi ne kowane musulmi ya bayar da sadaka Suka ce: Ya Manzon Allah Duk wanda bai same shi ba Yace Yana aiki da hannunsa Yana amfanar kansa da yin sadaka Suka ce Idan ba'a samu ba Yace Taimaka wa matsananciyar bukata Suka ce Idan ba'a samu ba Yace Bari ya yi da alheri Da kuma nisantar sharri Ita ce sadaka a gare shi Bukhari da Muslim ne suka ruwaito