Orchard Al-Huda Allah madaukakin sarki yace Duk wanda ya aikata sharri ko ya zalunci kansa sannan ya nemi gafarar Allah, zai sami Allah Mai gafara ne Mai jin kai An kar~o daga Anas bn Malik Allah Ya yarda da shi ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa Ina rantsuwa da wanda raina ke Hannunsa, ko kuma da wanda ran Muhammadu yake a hannunsa Idan kun yi zunubi har zunubanku sun cika sarari tsakanin sama da ƙasa Sannan ka nemi gafarar Allah zai gafarta maka Ina rantsuwa da wanda ran Muhammadu ke Hannunsa, ko kuma da wanda raina ke hannunSa Kuma dã ba ku yi zunubi ba, dã Allah Ya zo da mutãne mãsu laifi Sannan su nemi gafarar Allah kuma Ya gafarta musu Ahmed ne ya rawaito Amfani Kuma aka ce wa Al-Hasan Allah Ya yi masa rahama Shin dayanmu baya jin kunyar neman gafarar Ubangijinsa akan zunubansa? Sannan ya dawo, sannan ya nemi gafara, sannan ya dawo Sai ya ce Shaiɗan zai so ya yaudare ka da ikonsa Kar ka gajiya da neman gafara An ruwaito yana cewa: Ni ina ganin wannan ba komai ba ne face dabi’un muminai Wannan yana nufin cewa duk lokacin da mumini ya yi zunubi, ya tuba