Allah madaukakin sarki yace Kuma waɗanda suke ciyar da abin da Ya bãyar, kuma zukãtansu suka yi tsõron cħwa zuwa ga Ubangijinsu muke komawa. Waɗannan ne waɗanda suke gaugãwa zuwa ga ayyukan alhħri, kuma sũ ne a gabãninsu. Uwar Muminai A’isha, Allah Ya yarda da ita ta yi tambaya Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi game da wannan aya mai daraja Sai ta ce Ya Manzon Allah Suna bayar da abin da suke bayarwa, kuma zukatansu suna cikin tsoro. Shi ne mai yin sata, yana zina, yana shan giya Yana tsoron Allah Madaukakin Sarki Ya ce, Allah Ya jikansa da rahama A'a 'yar abokina Amma su ne masu yin sallah, da azumi, da sadaka Suna tsoron kada a karba daga gare su Waɗannan su ne waɗanda suke gaugãwa zuwa ga ayyukan ƙwarai