Sunnar Annabi ta tabbata Sanya hannu akan wurin zafi da addu'a An kar~o daga Othman bn Abi Al-Aas, Allah Ya yarda da shi Ya kai karar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ciwon da yake ji a jikinsa tun bayan da ya musulunta. Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce masa Ka sanya hannunka akan sashin jikinka da ke ciwo sannan ka yi Bismillah sau uku Kuma ka ce sau bakwai: Ina neman tsarin Allah da ikonSa daga sharrin abin da na samu, kuma ina yin hattara Muslim ne ya ruwaito shi