Hadisai arba'in akan falalar sadaka An kar~o daga Abdullahi xan Umar Allah Ya yarda da su ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce Lallai Allah yana da mutanen da ya kebance ni'ima domin amfanin bayinsa. Za a saka musu da abin da suka aikata Idan suka hana, sai ya kwace musu, ya mika wa wasu. Al-Tabarani da Al-Bayhaqi ne suka ruwaito, Albaniy ya inganta shi.