Sunnar Annabi ta tabbata atishawa tayi An kar~o daga Abu Hurairah, Allah Ya yarda da shi An kar~o daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya ce Idan ɗayanku ya yi atishawa sai ya ce: “Godiya ta tabbata ga Allah”. Bari ɗan'uwansa ko abokinsa ya gaya masa Allah ya jikansa da rahama Idan ya ce masa, Allah Ya yi maka rahama Sai ya ce, “Allah Ya yi muku jagora, Ya kuma daidaita hankalinku”. Bukhari ne ya ruwaito shi